Jam’iyyar NDC ta bayyana dalilin da ya sa take bukatar duk ’yan takararta, ciki har da na shugaban kasa Peter Obi, mataimakinsa Rabiu Musa Kwankwaso da sauran masu neman kujeru, su sanya hannu kan yarjejeniyar adawa da barin jam’iyya kafin a shiga zaben 2027.
Jam’iyyar adawar ta ce wannan tsari na da nufin kare nasarorin da ta samu a zabe da hana maimaita matsalar barin jam’iyya da ta raunana jam’iyyu da dama a shekarun baya.
Da yake jawabi a lokacin da aka kaddamar da tsarin a sakatariyar jam’iyyar ta kasa da ke Abuja a ranar Talata, Shugaban NDC na kasa, Moses Cleopas, ya ce kowane dan takara da ke son tsayawa takara a karkashin tutar jam’iyyar dole ne ya sa hannu kan takardar rantsuwa da ta daukar alhakin da ke dauke da ita na barin kujera idan ya tsallaka wata jam’iyya bayan ya ci zabe.
A cewar Cleopas, an yanke wannan hukunci ne a taron Kwamitin Zartaswa na Kasa NEC, kuma nufinsa shi ne karfafa da’a a jam’iyyar da tabbatar da zababun a karkashin jam’iyyar sun ci gaba da zama masu biyayya ga jam’iyyar da ta ba su dama.
Ya koka kan wata dabi’a da ke maimaituwa a siyasar Najeriya inda ’yan siyasa ke samun nasara a zabe a karkashin wata jam’iyya sannan daga baya su koma wata, sau da yawa jam’iyyar da ke mulki a kasa bayan sun hau mulki.
“Mutanen suna tsaya zabe kuma sun ci a karkashin jam’iyyu, amma da zarar an zabe su sai su watsar da jam’iyyar da ta ba su damar. Wannan ya zama babban kalubale a dimokuradiyarmu,” in ji shi.
Shugaban NDC ya ambaci abin da ya faru da Labour Party bayan zaben 2023 a matsayin daya daga cikin dalilan da suka sa suka dauki wannan tsari.
A cewarsa, mutane da dama da suka ci zabe a karkashin jam’iyyar Labour Party daga baya sun bar jam’iyyar, lamarin da ya raunana karfi da tasirinta na siyasa.
“Da wadancan zababun jami’an sun ci gaba da kasancewa a jam’iyyar Labour Party, da jam’iyyar ta fi karfi da ta ke da shi a yau. Wannan gaskiyar ce yasa ya zama wajibi jam’iyyu su sanya matakan kariya,” in ji shi.
Cleopas ya jaddada cewa zama dan jam’iyyar NDC lamari ne na ganin dama, amma ’yan takara dole ne su amince da bin ka’idojin jam’iyyar kafin a ba su tikiti.
Ya ce nasarar zabe mallakin jam’iyya ne ba na mutum ba, yana mai cewa duk wanda ya yanke shawarar barin NDC bayan ya ci zabe ya kamata ya bar kujerar da ya samu ta hanyar jam’iyyar.
“Idan ka tsaya takara a karƙashin NDC ka ci, nasarar jam’iyya ce. Idan ka zabi barin jam’iyyar, to kai ma ka bar abin da ka samu ta jam’iyyar,” in ji shi.
Don tabbatar da aiwatar da wannan tsari, gungun lauyoyin jam’iyyar sun shirya takardar rantsuwa da takardun daukar alhaki da duk ’yan takara dole ne su sa hannu kafin su shiga zabe.
Mai Ba da Shawara kan Harkokin Shari’a na NDC, Reuben Egwuaba, ya kare matakin, yana mai cewa jam’iyyun siyasa kungiyoyi ce ta sa kai da ke tafiya da ka’idojin da mambobinsu suka amince da su.
Ya ce Kundin Tsarin Mulki ya amince da jam’iyyun siyasa a matsayin hanyar da ’yan takara ke tsayawa zabe, kuma ya jaddada cewa zababun jami’ai na ci gaba da zama wakilan jam’iyyar da ta dauke su a duk tsawon mulkinsu.
Kaddamar da tsarin adawa da barin jam’iyyar ya zo ne a daidai lokacin da ake samun damuwa kan sake kulla alaka a siyasa kafin zaben 2027.
Ko da yake Obi, Kwankwaso da wasu manyan mutane basu samu halartar taron ba, ana sa ran tsarin zai shafi duk ’yan takarar NDC ba tare da banbancewa ba.












































