Hukumar dake shirya jarrabawar shiga manyan makarantun gaba da sakandire (JAMB), ta saki wani sabon sakamakon jarrabawar da dalibai suka rubuta a ranar Litinin, 20 ga watan Afrilu.
Kakakin hukumar ta JAMB, Fabian Benjamin ne ya sanar da sakin sakamakon a wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata. Duk da dai bai fadi adadin daliban da aka saki sakamakon na su ba.
Benjamin yace, daliban da suka rubuta jarrabawarsu a ranar Litinin za su yi duba sakamakonsu na jarrabawar, ta hanyar da aka saba.
A ranar Asabar din da ta gabata, hukumar ta JAMB ta saki sakamakon jarrabawar da aka rubuta a ranar Juma’a da Asabar na dalibai 1,264,940.
Tun da fari dai hukumar ta saki sakamakon dalibai 632,752 da suka rubuta jarrabawa a ranar Alhamis, wanda ya kai adadin dalibai 1,897,692 kafin ranar Litinin.
Dalibai da dama sun koka kan jinkirin da aka samu kafin sakin sakamakon jarrabawar da aka rubuta a ranar Juma’a, wanda hakan yasa suka asarar kudade da hukumar ke chaza yayin duba sakamakon.
Hukumar dai ta yi watsi da kiraye-kirayen da ake yi mata na maida wa daliban kudadensu, inda tace dama bata sanar da sakin sakamakon ba.













































