Yadda ƙorafe-ƙorafe ya tilastawa shugaban hukumar NAHCON yin murabus

NAHCON Chairman Prof Abdullahi Saleh Usman 750x400

Shugaban Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Usman, ya ajiye mukaminsa a yayin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce da rikice-rikicen cikin gida a hukumar.

Mataimakinsa na yada labarai, Ahmed Muazu, ya tabbatar da murabus din a daren ranar Litinin, amma bai bayar da cikakken bayani kan dalilan daukar matakin ba.

Muazu ya ce, “Eh, shugaban ya yi murabus. Wannan ne kawai zan iya tabbatarwa a yanzu.”

An nada Farfesa Usman a shekarar 2024 ta hannun Shugaba Bola Tinubu domin maye gurbin Jalal Arabi, wanda aka kora daga mukaminsa yayin da ake bincikensa kan zargin almundahana da kudaden da aka ware domin aikin hajjin shekarar 2024.

Tun bayan hawansa kan mukamin, wa’adin Farfesa Usman ya kasance cike da kalubale.

Babban aikin da ya fara jagoranta, wato shirya aikin hajjin shekarar 2025, ya fuskanci zarge-zargen kura-kuran kudi da matsalolin gudanarwa.

Rahotanni sun nuna cewa murabus din nasa ya biyo bayan wata takardar koke da kwamitin gudanarwar NAHCON ya mika wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda suka bukaci a cire shi daga mukamin bisa zargin saba ka’idoji da sauran munanan ayyuka.

Takardar koken, wadda dukkan mambobi 11 na kwamitin suka sanya hannu kuma aka rubuta ta a ranar 19 ga Janairu, 2026, ta samu taken Rashin amincewa da Shugaban Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON), Farfesa Abdullahi Saleh Usman.

Takardar ta ce matakin ya biyo bayan dogon lura da halayen cikin gida da kuma kokarin gyara da aka yi sau da dama, inda aka ce gazawar jagoranci ta janyo tabarbarewar amincewa, kwanciyar hankali da ingancin ayyukan hukumar.

Takardar ta zargi shugaban da rashin da’a wajen tafiyar da kudi, rashin gaskiya, da kashe kudade da bayar da kwangiloli ba tare da amincewar kwamitin ba, tare da wuce iyakokin kasafin kudi.

Takardar ta ce wadannan ayyuka sun saba dokokin tafiyar da harkokin kudi, tare da bayyana cewa shugaban na fuskantar bincike a hannun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC).

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here