Babban layin wutar lantarki na ƙasa ya faɗi

Blackout

Babban layin wutar lantarki na ƙasa ya fadi a yammacin ranar litinin, lamarin da ya sa wutar lantarki ta ragu ƙwarai a mafi yawan sassan ƙasar, bisa alkaluman rarraba wuta da kamfanonin rarraba wutar lantarki suka fitar da misalin ƙarfe uku da mintuna goma sha biyu na rana.

Bayanai daga kamfanonin rarraba wutar lantarki sun nuna cewa kamfanoni biyu ne kaɗai suka samu wuta a lokacin faɗuwar, inda kamfanin rarraba wutar lantarki na Ibadan ya samu megawatt 30, yayin da kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja ya samu megawatt 20.

Sauran kamfanonin rarraba wutar lantarki na Benin, Eko, Enugu, Ikeja, Jos, Kaduna, Kano, Port Harcourt da Yola duk sun samu megawatt sifili, abin da ke nuna katsewar wuta a manyan birane da yankuna daban-daban na ƙasar.

Jimillar wutar lantarki da aka rarraba a ƙasa baki ɗaya a lokacin ta tsaya ne a megawatt 50 kacal, wanda ya yi ƙasa da matakin aiki na yau da kullum kuma bai isa ya wadatar da gidaje, kasuwanci da muhimman ayyuka ba.

A shekarun baya-bayan nan, babban layin wutar lantarki na ƙasa ya sha fuskantar rushewa sau da dama, lamarin da ke haddasa katsewar wuta a faɗin ƙasa tare da jinkirin dawo da wutar.

A halin da ake ciki, kamfanin wutar lantarki na ƙasa NNG ya bayyana cewa ana ci gaba da aikin dawo da wutar lantarki.

Sai dai zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, kamfanin watsa wutar lantarki na ƙasa da ma ma’aikatar wutar lantarki ta gwamnatin tarayya ba su fitar da wata sanarwa ba kan musabbabin rushewar ko kuma lokacin da ake sa ran dawo da wutar lantarki.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here