QGwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa a yanzu za a yi jana’izar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Talata 15 ga Yuli, 2025, a mahaifarsa ta Daura.
Allah ya yi wa tsohon shugaban Najeriya rasuwa a ranar Lahadi, 13 ga Yuli, 2025, a wani asibiti a birnin Landan na kasar Birtaniya.
Gwamna Radda ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Katsina ranar Litinin.
“Tsarin binne mahaifinmu, wanda ya rasu jiya a Landan, mun yi shawarwari da iyalai da mutanen da ke kusa da shi a Landan.
“Mun yanke shawarar cewa gawar zata isa Katsina da rana tsaka kuma za a yi jana’izar a Daura da misalin karfe 2 na rana,” in ji Gwamna Radda.













































