A yau Alhamis ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar da wasu ayyuka guda uku a garin Kafanchan hedikwatar karamar hukumar Jema’a a jihar Kaduna.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ruwaito cewa, hanyoyin sun hada da titin Katsina, titin Dan Haya da titin fadar sarki, wanda aka gina a karkashin shirin sabunta biranen Kafanchan na gwamnatin jihar.

A karkashin shirin sabunta birane na gwamnatin jihar, an sake gina tituna 21 masu tsawon kilomita 26.3 ko dai an sake gina su, ko kuma a fadada su ko kuma aka yi su biyu a garin Kafanchan, kan kudi naira biliyan 12.8.

Haka kuma shugaba Buhari ya kaddamar da gadar sama dake Kawo akan titin Kaduna zuwa Kano, wadda aka gina akan kudi Naira Biliyan 7.

Daga nan Shugaban kasa ya wuce zuwa filin wasa na Murtala Square domin ganin yadda aka gyara shi ya koma na zamani.









































