Hukumar kula da babban birnin tarayya Abuja (AMMC) na hukumar gudanarwar babban birnin tarayya Abuja ta bayar da umarnin rusa wasu dogwayen benaye 24 da aka gina ba bisa ka’ida ba a kan hanyar ruwa a gundumar Guzape da ke Abuja.
Kodinetan AMMC, Cif Felix Obuah, ne ya bayar da wannan umarni a rangadin da suka kai sassa daban-daban na Abuja a ranar Litinin, tare da wasu jami’an hukumar.
Obuah ya bayyana cewa Cityscape Estate ne ya gina gine-ginen akan Plot 4851 ba tare da izini ba.
Ya kuma bayyana ginin a matsayin cin zarafi ga ka’idojin tsare-tsaren birni sannan ya sha alwashin cewa za a cire gine-ginen ne domin ya zama izna ga wasu.
Ya yi gargadin cewa jami’an AMMC da aka samu da hannu wajen amincewa ko sa ido kan gine-ginen ba bisa ka’ida ba, za su fuskanci hukuncin ladabtarwa, yana mai jaddada cewa majalisar ba za ta kara amincewa da sakaci ko yin zagon kasa ba.
Karanta: Rashin zuwa makaranta: Kaduna za ta horar da jami’an kula da makarantu su 8,700
Mahukuntan sun ba da wa’adin makwanni biyu domin kawar da duk wani sabani da son rai.
Daraktan kula da ci gaban kasa, Mista Mukhtar Galadima, ya bayyana cewa tun da farko an ware wa ma’aikacin filin ne kusa da rukunin gidajen gwamnatin tarayya da ke yankin.
Shugaban hukumar hana fasa kwauri na FCT, Mista Gabriel Musa, ya bayyana cewa yayin da gine-gine 18 kacal aka amince da su, wanda kuma aka tarar ya gina 42, wanda ya ninka adadin da aka yarda.
A martanin da ya mayar, mamallakin wajen Kadiri Obaidi, ya amince da laifin kuma ya karɓi alhakin, yana danganta wasu ci gaban da ba a ba da izini ba ga masu biyan kuɗi.
Majalisar ta amince da bukatarsa ne da sharadin cewa za a cire duk wasu gine-ginen da ba a ba su izini ba ba tare da ko sisi ga gwamnati ba. (NAN)