Zulum ya biya Naira miliyan 5 don daukan nauyin karatun wani hazikin yaro mai Shekara 13 da ya kwaikwayi ginin gadar sama a Maiduguri

Musa Sani Borno 1
Musa Sani Borno 1

Gwamna Babagana Zulum na jihar Barno ya bada Naira miliyan biyar ga wata makaranta mai zaman kanta domin daukar nauyin karatun Musa Sani, yaro dan shekara 13 mai hazaka a Barno wanda yai amfani da laka ya kwaikwayi ginin gadar sama ta farko a jihar.

gwamnan ya biya kudin ne ga makarantar Golden Oliver Academy, Maiduguri domin daukar nauyin karatun Musa daga Firamare har kammala babbar sakandare.

A dai cikin kwanakin nan ne hankalin Zulum ya kai kan Musa bayan ya yi amfani da laka ya gina gadar sama da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya kaddamar a watan Disamba a cikin garin Maiduguri, Zulum ya yi sha’awar basirar da yaron keda ita, hakan yasa gwamnan ya nemi ganin iyayen yaron kuma ya bada tallafin karatun don inganta bisirar sa

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here