Aƙalla mutum ashirin ne suka mutu sakamakon wani rikicin ƙabilanci da ya ɓarke tsakanin ƙabilun Wurkunawa da kuma Karimjo a ƙaramar Hukumar Karim Lamido ta jihar Taraba.
An kuma ƙona gidaje da dama da asarar dukiya mai dimbin yawa.
Tashin hankalin ya samo asali ne kan batun sarautar gargajiya a yankin.
A cikin makon da ya gabata ne gwamnan jihar ta Taraba Darius Ishaku ya bai wa Alhaji Yakubu Abubakar Haruna sanda a matsayin sabon sarki a masarautar Wurkum da ke Karamar Hukumar Karim Lamido a jihar Taraba.













































