Tsohon gwarzon Dan wasan dambe na Duniya, da ya yi murabus Dan Kasar Amurka Floyd Mayweather Junior, ya kawo ziyara Nigeria.
A ziyarar ta sa ranar Litinin 09 ga Mayu 2022, ya gana da ministan sufuri Rotimi Amaechi, tare da yin alkawarin samar da makarantar wasan dambe a Kasar.
Tsohon zakaran wasan ajin masu nauyin ya bayyana hakane yayin tattaunawar sa da manena labarai a birnin tarayya Abuja.
Ana sa ran tsohon Dan wasan zai tattauna da jami’an hukumar wasan Dambe ta Najeriya domin bada shawarwari tare da kulla Alaka don habakka wasan a fadin Kasar.













































