Zaɓaɓɓen gwamnan Kano, Abba Kabir ya shawarci magoya bayan sa da su tayashi da addu’a domin samun Nasara a gwamnatin sa.
Ya ce addu’a ce kadai zata ta bashi damar kawo karshen matsalolin da jihar Kano ke fuskanta a halin yanzu.
Hakan na dauke cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Zaɓaɓɓen gwamnana, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya sawa hannu.
Ya kuma shawarci magoya bayyan sa da suke shirin yin tattaki daga wasu jihohin zuwa kano, domin nuna goyan bayan su gareshi, da su da kata da yin tattakin, kawai addu’ar su yake nema.













































