Shugaban Hukumar Karbar Korafe-Korafe da Yaki da Cin Hanci ta Jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimingado, wanda rundunar ‘yan sanda ta sashin IGP suka kama suka tsare a Zone One Kano, an sake shi.
An kama Rimingado ne ranar Juma’a saboda kwace wasu kadarori da ake zargin suna da alaka da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje.
Majiyoyi sun tabbatar wa SolaceBase cewa an saki Rimingado bisa beli kan amincewa da kansa bayan ya rubuta bayani da misalin karfe 10:45 na dare ranar Juma’a.
An tambaye shi kan kadarorin da aka kwace a binciken zargin karkatar da sama da Naira biliyan hudu daga hannun tsohon shugabar KASCO, Bala Muhammed Inuwa, da wasu mutane uku, in ji majiyar.
Haka zalika, an ce kadarorin da aka kwace daga hannun Bala Inuwa na da alaka da Ganduje, kuma tsohon shugabar ya bayyana cewa babu wanda zai iya kwace kadarorin daga hannunsa.
Sai dai an bukaci Rimingado ya bayyana a hedkwatar ‘yan sanda ta Abuja ranar Litinin domin karin bincike. Duk kokarin SolaceBase na jin ta bakinsa ya ci tura, domin wayarsa a kashe take.