A ranar Lahadin nan ne ‘Yan bindiga suka sace Charles Mato Daka, wani basaraken garin Gindiri dake karamar hukumar Mangu ta Jihar Filato.
Mai magana da yawun rundunar Operation Safe Haven ta sojojin Najeriya a Filato, Manjo Ishaku Takwa, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya shaida wa manema labarai a Jos cewa an yi garkuwa da Mato ne a gidansa dake Gindiri.
Ya ce an tura jami’an tsaro zuwa wurin da abin ya faru domin bin sawun maharan.
“Dakarun OPSH da ke Gyambus a Mangu sun tafi zuwa yankin. Suna kan hanyar bin sawun masu garkuwa da mutanen,” in ji Takwa.
NAN













































