Wanda ake zargi da safarar mutane ya kashe kansa, yayin da NAPTIP ke tsare dashi

NAPTIP LOGO
NAPTIP LOGO

Rundunar ‘yan sada sun tabbatar da mutuwar wani dan shekara 39, wanda ya kashe kansa, yayin da hukumar yaki da safarar dan’adam NAPTI ta garkameshi.

Wanda ake zargin ankamashine a karamar hukumar Ikeja da ke jihar Lagos, bisa zargin sa da safarar dan Adam.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Lagos, Benjamin Hundeyin ya tabbatar da faruwar al-amarin ranar Litinin, inda yace an garzaya da gawar asibiti.

Ya kuma tabbatar da cewa rudunar ‘yan sandan zata cigaba da bincike akan faruwar lamarin.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here