Yau shugaban kasa Muhamadu Buhari zai kama hanyar zuwa Dakar, babban birnin Senegal, don halartar taron ƙungiyar samar da ci gaban ƙasa da ƙasa ta IDA
Bayanin hakan na dauke cikin wata sanarwa da maiataimakawa shugaban kasar kan al-amuran yada labarai, Mallam Garba Shehu, ya fitar.
Sanarwar ta kara da cewa ana sa ran dawowar Buharin gida Najeriya ranar Alhamis.
Shugaban kasar zai sami rakiyar manyan manyan jami’an gwamnatin Najeriya.













































