Sarki Charles III ya yabawa gudummawar ‘yan Najeriya da ke zaune a kasar ta Birtaniya.
Sarkin, wanda ya yi magana a wata liyafar sarauta da aka shirya domin karrama shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu a ranar Laraba, ya jaddada irin tasirin ‘yan Najeriya a cikin al’ummar Birtaniya, yana mai bayyana su a matsayin ginshiki ga ci gaban kasa da kirkire-kirkire.
Wannan liyafar na daga cikin shirye-shiryen ziyarar aiki ta kwanaki biyu da Tinubu ke yi zuwa kasar.
Ya bayyana cewa ‘yan Najeriya na taka rawa sosai a rayuwar Birtaniya, inda suke bayar da gudummawa a fannoni daban-daban.
Sarkin ya kara da cewa ‘yan Najeriya na samun nasara a manyan matakai a bangarorin kasuwanci, fasaha, ilimi, shari’a, kimiyya, wasanni, adabi da kuma fannin fasaha.
Ya ce a cikin mu’amalarsa da al’ummar ‘yan Najeriya, ya hadu da mutane da dama da yake kira jarumai masu tawali’u, wadanda ke bayar da gudummawa sosai a makarantu, kasuwanci, cibiyar kula da lafiya ta kasa da jami’o’i.
Ya kuma bayyana cewa ya hadu da matasa da dama da suka samu nasara ta hanyar ayyukan gidauniyar sarki wadda ta kwashe shekaru 50 tana aiki.
Sarkin ya kuma tuna da wani taro da aka yi kwanan nan a St. James’s Palace, inda ya karbi bakuncin ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje.
Ya ce ya shirya musu wani taron cin abinci na shinkafar jollof da shayi, inda aka tabbatar masa cewa shinkafar jollof din ita ce mafi inganci kuma ta Najeriya ce.
A bangaren girmamawar soja, Tinubu ya fara ziyararsa ta kwanaki biyu da cikakken girmamawa na al’ada a ranar Laraba.
An tarbe shi da cikakken bikin gwamnati wanda ya hada da dakarun girmamawa da harbe-harbe na al’ada, alamar kyakkyawar dangantakar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Birtaniya.
Ziyarar shugaban kasar ta hada da ganawa da manyan jami’an Birtaniya da kuma tattaunawa da ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje.
An tsara ziyarar ne domin karfafa dangantakar kasashen biyu, bunkasa kasuwanci da zuba jari, da kuma kara hadin gwiwa a fannoni masu muhimmanci kamar tsaro da ilimi.
Kasancewar ‘yan Najeriya da yawa a Birtaniya ana kallon sa a matsayin wata muhimmiyar dama wajen kara dankon zumunci tsakanin kasashen biyu.










































