Ƙungiyar Masu Haƙar Ma’adinai ta ƙasa (MAN) ta ce hana ayyukan haƙar ma’adinai a ƙasar ba shi ne mafita ga matsalolin tsaro da ake fuskanta ba.
Kungiyar ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da shugaban ta na ƙasa Dele Ayankale da sakataren ta na ƙasa Sulaiman Liman suka rattaba wa hannu a ranar Litinin a Abuja.
Kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN ya tuna cewa ƙungiyar gwamnonin jihohin Arewa a baya-bayan nan ta nemi a dakatar da ayyukan haƙar ma’adinai na tsawon watanni shida bayan sace ’yan makaranta da kashe-kashe da suka faru a wasu jihohi.
Sun bayyana haramtacciyar hanyar haƙar ma’adinai a matsayin muhimmin abin da ke haifar da rashin tsaro, tare da cewa dakatar da ayyukan zai ba da damar gudanar da cikakken bincike da sake tantance dukkan lasisin hakar ma’adinai tare da tuntubar gwamnatocin jihohi.
Karanta: Zaman lafiya ya dawo a ƙauyen Dangoro bayan masu gonaki da gwamnatin jihar Kano sun cimma matsaya
Sai dai, shugaban MAN ya ce haramtacciyar hakar ma’adinai kaɗai aka danganta da taimaka wa ta’addanci da sauran matsalolin tsaro, ba ayyukan halal ba, kuma ya yi Allah wadai da cewa dakatarwar za ta cutar da masu aikin halal yayin da za ta bai wa haramtattun ayyuka damar ci gaba.
Ayankale ya bayyana cewa dakatarwar da aka yi a baya kan ayyukan hakar ma’adinai a matsayin dabarar rage rashin tsaro ba ta haifar da sakamako mai kyau ba, kamar yadda aka gani a haramcin ayyukan hakar ma’adinai a Zamfara a 2019, yana mai cewa illolin sun fi amfani.
Ya ce, maimakon haka, ayyukan ’yan ta’adda, sace mutane da ta’addanci sun ƙaru a jihar kuma sun bazu zuwa jihohin makwabta kamar Katsina, Kaduna, Neja, da Kebbi, da sauransu.
Ya jaddada cewa dakatarwar za ta kasance rashin adalci kuma babban cikas ga masu hakar ma’adinai na halal da ma’aikatansu, wanda zai haifar da yawan rashin aikin yi, ƙara talauci mai yawa a fannoni daban-daban, tare da tsananta rashin tsaro.
Ayankale ya kara da cewa wannan shirin gaba ɗaya ya saba da rubutu da kudirin Kundin Tsarin Mulki, wanda ya tanadi ikon sarrafawa da kula da ma’adinai a cikin Jerin Dokokin Kasa ta Musamman.
Ya roki shugaban ƙasa da ya yi la’akari da cewa wannan haramcin na iya ƙara yawan mutanen da za su shiga ayyukan ta’addanci. (NAN)













































