Malami ya magantu dangane da rade-radin ya yi murabus daga mukamin minista 

Abubakar Malami 1
Abubakar Malami 1

Babban Lauyan gwamnatin tarayya (AGF) kuma ministan shari’a, Abubakar Malami (SAN), a ranar Alhamis ya ce bai yi murabus daga mukaminsa ba kamar yadda wasu kafafen yada labarai suka ruwaito.

Ya bayyana haka ne a taron manema labarai na shekara-shekara da kungiyar masu aiko da rahotanni shari’a ta kasa (NAJUC) ta shirya a Abuja.

Ministan ya ce: “Masu yada labaran basu kware ba, domin kuwa ko a cikin satin nan an ga Malami da aka ce ya yi murabus a ofis yana gudanar da ayyukansa da suka hada da halartar taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya a Laraba, inda ya yi hira da ‘yan jarida.

Ya yi kira ga ‘yan jarida da su guji yada “labaran karya, bata suna, tada zaune tsaye, kalaman kyama, da tsokana a cikin rahotonsu.

“Tsarin doka mai inganci na iya zama babban zaɓi. Lokaci ya yi da za mu haɓaka ilimin kafofin watsa labarai ga ’yan Najeriya don jin daɗin bincikar gaskiya da tabbatar da bayanai,” in ji Ministan.

An shirya taron ne don haɓaka ƙwarewar masu aiko da rahotanni na shari’a da sauƙaƙe sauke nauyin da ke kansu na ‘yan jarida da kuma muhimman al’umma.

AGF ya ce, burin Gwamnatin Tarayya ne na ganin ta magance hukunce-hukunce masu cin karo da juna tare da neman sanin yakamata a harkar shari’a.

 

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here