Kotun Ƙolin Najeriya ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar ADC ɓangaren Sanata David Mark.
A hukuncin da kotun ta yanke ƙarƙashin mai shari’a Mohammed Lawal Garba, ta ce masu ƙarar su koma babbar kotun tarayya domin ci gaba da shari’ar da ake yi.
Alƙalan sun kuma yi watsi da hukuncin da kotun ɗaukaka ƙara ta yanke na cewa a tsaya inda ake da cire sunan shugabancin ADC ɓangaren David Mark daga shafin INEC.












































