Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, a ranar Laraba, ta yi watsi da karar da ke neman korar Mista Ola Olukoyede a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC).
Mai shari’a Obiora Egwuatu, a cikin hukuncin da ya yanke, ya kori karar ne bisa hujjar cewa mai neman ba shi da hurumin shigar da karar.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya NAN ya ruwaito cewa wani lauyan dake zaune a Abuja, Mista Victor Opatola, ya shigar da karar shugaban kasa Bola Tinubu kan nadin Olukoyede a matsayin shugaban EFCC.
Opatola, a cikin karar ya kalubalanci sahihancin nadin ne bisa hujjar cewa Olukoyede bai cika shekarun aikin da doka ta bukata na ofishin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ba.
Ya sanya sunayen Shugaban Najeriya, Majalisar Dokoki ta kasa, Atoni-Janar na Tarayya (AGF) da Olukoyede a matsayin masu amsa na 1 zuwa na 4, a cikin karar mai lamba: HC/ABJ/CS/1403/2023.
Sai dai wadanda ake kara sun roki kotun da ta yi watsi da karar saboda rashin cancantar su.
Olukoyede, wanda Olumide Fusika, SAN, ya wakilce shi a ranar da aka dage sauraron karar, ya kalubalanci hurumin shari’a na wanda ya shigar da karar da ya shigar da karar a matakin farko.