Kotu ta aike da budurwa zuwa Kirikiri bisa cin zarafin dan sanda a Legas.

Wata kotu ta bada umarnin tsare wata budurwa mai suna Olufumilayo Brioluwa a gidan yari na Kirikiri bisa laifin cin zarafin wani dan sandan Najeriya a jihar Legas.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Benjamin Hundeyin ne ya bayyana hakan a wani sakon Twitter da ya wallafa.

A cewar Hundeyin, Brioluwa ya farwa dan sandan ne a yankin Ogombo da ke jihar.

Ana ci gaba da tsare ta a gidan gyaran hali na Kirikiri har zuwa ranar 6 ga watan Yuni lokacin da za a kaita kotu.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here