KNUPDA: ‘Yan kasuwa 5,000 za su rasa shagunansu a jihar Kano

Abba Kabir Yusuf, KNUPDA, 'Yan kasuwa, rasa, shaguna, jihar, Kano
Kimanin 'yan kasuwa 5,000 a kewayen masallacin Idi da ke kan titin IBB a jihar Kano ne za su yi asarar shagunansu sakamakon sanarwar dakatar da su da Hukumar...

Daga: Sunusi A. Dantalata Fagge

Kimanin ‘yan kasuwa 5,000 a kewayen masallacin Idi da ke kan titin IBB a jihar Kano ne za su yi asarar shagunansu sakamakon sanarwar dakatar da su da Hukumar Tsare-tsare da Raya Birane ta Jihar Kano (KNUPDA) ta yi musu.

Shugaban kungiyar ‘yan kasuwar Yakubu Muhammad ne ya bayyana haka a ranar Talata yayin wata ganawa da manema labarai.

KNUPDA ta bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga ‘yan kasuwa a masallacin da ke kan titin IBB a cikin babban birnin Kano da su bar yankin ko kuma su fuskanci fushin doka.

Karin labari: Hukumar NRC ta bayyana lokacin da jirgin kasan Kaduna zuwa Kano zai fara aiki

Muhammad ya bayyana cewa shekaru 18 da suka gabata Marigayi Galadima na Kano, Alhaji Tijjani Hashim ne ya raba musu wurin ta hannun Masarautar.

“An ware wurin ne ga mambobinmu domin duba laifuka daban-daban kamar satar waya da sauran ayyuka da ake tafkawa a wuraren,” inji shi.

Ya ce gwamnatocin da suka gabata a jihar sun ga ya zama dole a bar ‘yan kasuwar su ci gaba da gudanar da ayyukansu a yankin.

Karin labari: Zan Aike Wa Majalisa Ƙudiri Game Da Sabon Mafi Ƙarancin Albashi — Tinubu

Muhammad ya ce ’yan kasuwar ba su fahimci dalilin da ya sa gwamnati ke aika musu kaya ba duk da cewa suna bin doka da oda kuma suna ba da gudunmawar kudaden shiga da jihar ke samu a cikin gida.

“Har yanzu muna kokarin ganin mun shawo kan hakikanin laifin da muka aikata wanda ya sa KNUPDA ta fatattake mu daga inda muke gudanar da sana’o’inmu na halal domin kula da iyalanmu.

“Mun goyi bayan wannan gwamnati. Mun zabe ta a lokacin zaben 2023. Mafi kyawun ƙarfin da wannan gwamnati za ta iya ba mu shi ne ta ba mu damar ci gaba da kasuwancinmu a Masallacin Idi,” in ji shi.

Karin labari: Majalisar wakilan Najeriya ta nada sabbin shugabannin kwamitoci

Ya kuma bukaci Gwamna Abba Kabir Yusuf da su shiga tsakani domin ceto sana’o’insu daga rugujewa.

Da aka tuntubi wata majiya a KNUPDA da ta nemi a sakaya sunanta ta tabbatar da cewa hukumar ta umarci ‘yan kasuwar da su bar wurin saboda suna mamaye wurin ba bisa ka’ida ba.

“KNUPDA na ganin ‘yan kasuwar ba su nemi izini daga gare ta ba kafin su fara kasuwanci a can. Don haka ne hukumar ta bayar da sanarwar janyewar, suna harkokin su ne ba bisa ka’ida ba a wurin” a cewar majiyar kamar yadda NAN ta tabbatar.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here