Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi ta tabbatar da tsare jami’anta uku bisa zargin kashe wani Abubakar Auwal, wanda ya mutu a hannun ‘yan sanda bisa wasu dalilai da ake zargi.
A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar a ranar Asabar, ya ce lamarin ya faru ne biyo bayan korafin satar wasu kayan tireloli da aka kai hedkwatar ‘yan sanda da ke Jega a ranar 15 ga Afrilu, 2025.
Sanarwar ta ce, “Marigayin, Abubakar Auwal, an kama shi ne a matsayin wanda ake zargi da aikata laifin.
“A yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike, an ruwaito Auwal ya fadi a gidan yari a safiyar ranar 16 ga watan Afrilu, inda aka garzaya da shi babban asibitin Jega.
“Rahotanni sun ce ya mutu a daren da misalin karfe 10:00 na dare.”
Sanarwar ta ci gaba da cewa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Bello Sani, ya ba da umarnin gudanar da bincike mai zurfi daga hukumar binciken manyan laifuka ta jihar (SCID).
A halin da ake ciki, rundunar ba ta bayyana sunayen jami’an da aka kama ba amma ta tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike.












































