Kebbi: ‘Yan sanda sun tsare wasu jami’ai uku kan mutuwar wani da ake zargi

Police badge

Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi ta tabbatar da tsare jami’anta uku bisa zargin kashe wani Abubakar Auwal, wanda ya mutu a hannun ‘yan sanda bisa wasu dalilai da ake zargi.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Nafiu Abubakar ya fitar a ranar Asabar, ya ce lamarin ya faru ne biyo bayan korafin satar wasu kayan tireloli da aka kai hedkwatar ‘yan sanda da ke Jega a ranar 15 ga Afrilu, 2025.

Sanarwar ta ce, “Marigayin, Abubakar Auwal, an kama shi ne a matsayin wanda ake zargi da aikata laifin.

“A yayin da ake ci gaba da gudanar da bincike, an ruwaito Auwal ya fadi a gidan yari a safiyar ranar 16 ga watan Afrilu, inda aka garzaya da shi babban asibitin Jega.

“Rahotanni sun ce ya mutu a daren da misalin karfe 10:00 na dare.”

Sanarwar ta ci gaba da cewa, kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Bello Sani, ya ba da umarnin gudanar da bincike mai zurfi daga hukumar binciken manyan laifuka ta jihar (SCID).

A halin da ake ciki, rundunar ba ta bayyana sunayen jami’an da aka kama ba amma ta tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here