KAROTA ta kama direban motar da ya taka fulawar da ake kawata titunan birnin Kano

d25585ed 244b 4522 b71c e5facc1ca645
Hukumar kula da zurga zurgar ababen hawa da kiyaye dokokin hanya ta jihar Kano KAROTA ta kama direban wata motar gida saboda zarginsa da karya dokar tuki.
Hukumar ta karota ta kama direban ne akan titin Murtala Muhammad dake birnin Kano bayan ya tsallaka titi ta wajen da bai dace ba ,tare da taka fulawar titi da gwamnatin Kano ta kawata titin da su.
A wata ganawarsa da manema labarai maimagana da yawun hukumar ta KAROTA Malam Abubakar Ibrahim Sharada yace direban ya karya dokar hanya kuma za’a gabatar dashi a gaban kotu domin zama izinina ga masu kokarin karya dokar tuki a kan hanya.
Yaja kunne direbobi da su guji karya dokar hanya,yana mai cewa hukumar ta KAROTA ba zata zura idanu ba.
An zargin Direban da yiwa yan karota din gadara.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here