Hukumar Zabe ta Kasa ta soke zabe a rumfunan zabe 13 a Karamar Hukumar Tudun Wada ta Jihar Kano.
Hukumar ta kuma ba da umarnin a sake zaben da aka gudanar a akwatunan kamar yadda ta sanar a ranar Alhamis.
Baturen zaben kujerar dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Doguwa da Tudunwada, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai, ya sanar cewa babu wanda ya lashe zaben.
(Aminiya)













































