Hukumar NAHCON ta tsawaita rajistar aikin Hajjin 2025

NAHCON Chairman Prof Abdullahi Saleh Usman sabo 750x430

Shugaban hukumar kula da aikin Hajji na kasa (NAHCON) Farfesa Saleh Usman, ya sanar da tsawaita wa’adin rajistar aikin Hajjin 2025 zuwa ranar 10 ga Fabrairun 2025.

A cewar wata sanarwa mai dauke da sa hannun mataimakiyar daraktar yada labarai ta NAHCON, Fatima Sanda Usara tace, matakin ya biyo bayan roko da aka yi a madadin maniyyatan da suka kasa kammala rajistar su kafin wa’adin da aka bayar tun ranar 31 ga watan Janairun 2025.

A yayin da yake sanar da tsawaita wa’adin a taron da suka gabatar a Zoom tsakanin NAHCON da masu ruwa da tsaki a aikin Hajji a daren ranar Talata, shugaban ya bukaci sakatarorin zartaswa na hukumar jin dadin alhazai na jihohi da su baiwa hukumar hadin kai domin ganin sun mika kudaden a kan lokaci, inda ya ce kudaden na da matukar muhimmanci wajen samun masauki a kan kari.

Labari mai alaƙa: NAHCON ta nemi CBN ta cire kashi 2% na kudaden Alhazai

“Yana da mahimmanci a lura cewa Saudiyya ta sanya ranar 14 ga Fabrairu, 2025, a matsayin wa’adin da aka kulla yarjejeniya, wannan yana nufin duk abin da za a biya dole ne ya isa ga asusun da aka keɓe a Saudi Arabia kafin wannan ranar don tantance shi”.

Usara ta kuma bayyana cewa, masu ruwa da tsaki sun amince da gudanar da tarukan tattauna batutuwa aikin hajjin ta Zoom akai-akai har sai an kammala dukkan shirye-shirye.

A cewar sanarwar, wani muhimmin batu da aka tattauna a kai shi ne shawarar da babban bankin kasar CBN ya bayar na bayar da alawus-alawus din tafiye-tafiye ta hanyar katin kiredit, wanda da yawa daga cikin mahalarta taron suka nuna adawa da irin wahalar da zai iya haifar wa alhazai.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here