A safiyar yau Talata Mataimakin Shugaban kasa Farfesa Yemi Osibanjo ya iso jihar Kano domin halartar taron tunawa marigayi Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sakoto.
Gwamnan jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje shine ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar zuwa filin jirgin sama na Malam Aminu Kano don taro Mataimakin Shugaban kasa da tawagar sa.
Taron wanda aka saba gudanarwa duk shekara zai gudana ne a dakin taro na Coronation Hall dake fadar gwamnatin jihar Kano.
![]()
![]()
![]()
Hotuna daga Abubakar Aminu Ibrahim, Babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kano kan kafafafen yada labarai na zamani














































