Rikicin APC a Kano: Kotun Daukaka Kara ta dage sauraren karar

Ibrahim Shekarau and Abdullahi Ganduje new 1
Ibrahim Shekarau and Abdullahi Ganduje new 1

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta dage karar da bangaren Gwamna Abdullahi Ganduje na jam’iyyar APC a Kano ya shigar da bangaren Sanata Ibrahim Shekarau zuwa ranar Juma’a 21 ga watan Janairu domin ci gaba da sauraren karar.

Wannan kara dai na kalubalantar shugabancin jam’iyyar APC a Kano wanda wata babbar kotu a babban birnin tarayya Abuja ta amince da zaben shugabannin jam’iyyar na mazabu dana jiha wanda bangaren Sanata Ibrahim Shekarau ya gudanar, inda aka tabbatar da Ahmadu Haruna Dnzago a matsayin shugaba, yayin da kotun ta yi watsi da zaben da bangaren gwamna Ganduje ya yi wanda suka ayyana Abdullahi Abbas a matsayin shugaba.

Muna tafe da cikakken bayani nan gaba.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here