Kotun daukaka kara da ke Abuja ta dage karar da bangaren Gwamna Abdullahi Ganduje na jam’iyyar APC a Kano ya shigar da bangaren Sanata Ibrahim Shekarau zuwa ranar Juma’a 21 ga watan Janairu domin ci gaba da sauraren karar.
Wannan kara dai na kalubalantar shugabancin jam’iyyar APC a Kano wanda wata babbar kotu a babban birnin tarayya Abuja ta amince da zaben shugabannin jam’iyyar na mazabu dana jiha wanda bangaren Sanata Ibrahim Shekarau ya gudanar, inda aka tabbatar da Ahmadu Haruna Dnzago a matsayin shugaba, yayin da kotun ta yi watsi da zaben da bangaren gwamna Ganduje ya yi wanda suka ayyana Abdullahi Abbas a matsayin shugaba.
Muna tafe da cikakken bayani nan gaba.













































