Hukumar Jin dadin alhazai ta jihar kano ta tabbatar da rasuwar wata mahajjaciya mai suna Hadiza Isma’il, yar asalin karamar hukumar Madobi a kasar Saudiyya.
Hadiza Isma’il, daga karamar hukumar Madobi ta rasu a ranar Litinin da misalin karfe 3:15 na rana agogon Saudiyya bayan ta yi fama da gajeruwar rashin lafiya, in ji sanarwar da ga Sanusi Bature Dawakin-Tofa, shugaban tawogar manema labarai na Hajjin bana.
Sanarwar ta ce an kai matar, mai shekaru 58 a asibitin NAHCON domin jinyar zazzabi kafin a kai ta asibitin Sarki Abdulaziz dake Makka inda aka tabbatar da rasuwarta.
Tuni dai aka binne ta a garin Makka bayan sallar jana’iza a masallacin Harami na Makkah.
Babban Daraktan Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano Alhaji Laminu Rabiu Danbappa ya mika ta’aziyyar hukumar ga iyalan mamaciyar a madadin gwamnan jihar Kano, ya kuma yi addu’ar Allah ya jikanta da rahama ya kuma baiwa iyalai hakurin jure rashin.