Gwamnatin Jihar Kano ta sake tabbatar da yinkurinta wajen magance lalacewar muhalli, hadarin ambaliyar ruwa da matsalolin zaizayar kasa a unguwannin da abin ya shafa.
Kwamishinan Ma’aikatar Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi, Dr. Dahiru Muhammad Hashim ne ya bayar da wannan tabbaci a ranar Juma’a yayin ziyarar duba aikin da ya kai wurin da ke fama da zaizayar kasa, Bulbula Gayawa a Kananan Hukumomin Nasarawa da Ungogo na Kano.
Ziyarar ta kasance wani bangare na ayyukan bikin Ranar Muhalli ta Duniya na bana da ke gudanarwa a fadin duniya a ranar 5 ga Yuni a karƙashin shirin Majalisar Dinkin Duniya domin wayar da kan jama’a kan kare muhalli.
Dr. Hashim ya ce ziyar ta kasance ta aunawa da gadawa wadda aka yi niyya domin tantance ayyukan da ake yi na magani a karkashin gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf, musamman kokarin da aka mayar da hankali kan dakile ambaliyar ruwa da zaizayar kasa.
A cewarsa, wurin da ke zaizayar kasa na Bulbula Gayawa ya kasance daya daga cikin matsalolin muhalli mafi tayar da hankali a jihar, wanda ya kai sama da kilomita 4 kuma ya shafi al’ummomin da ke kewaye da suka dade suna fama da wannan matsala na tsawon shekaru.
Ya bayyana cewa duk da an dade ana shakkar aikin saboda girma da rikitarwar sa, an fara aikin gine-gine a hukumance kusan shekara guda da ta gabata kuma tun daga lokacin an samu kaiwa ga matakin ci gaba mai mahimmanci. Ya ce, “Wannan al’umma ta dadd tana jiran wannan aikin, a lokacin yakin neman zabe, Maigirma Gwamna ya yi alkawarin magance wannan matsala, kuma yau muna ganin ci gaba na gaske a kasa.”
SolaceBase ta ruwaito cewa kwamishinan ya bayyana wurin zaizayar a matsayin abu mai hadari ba hadarin kadai muhalli ba, har ma da na zamantakewa da tsaro, inda ya ambaci abubuwan da suka faru na ambaliya, asar rayuka, hana zirga-zirga, da sauran matsalolin al’umma. Ya tuna cewa yankin ya taba yin rikodin asar yara masu radadi sakamakon abubuwan da suka shafi zaizayar kasa.
Dr. Hashim ya kuma bayyana damuwa kan zubar da shara ba bisa ka’ida ba cikin magudanan ruwa, inda ya bayyana shi a matsayin babbar barazana ga dorewar aikin. Ya yi gargadin cewa irin waɗannan ayyuka na iya kawo cikas ga ƙoƙarin gwamnati idan al’umma ba su magance shi cikin gaggawa ba, inda ya yi kira ga ƙarin haɗin kai don kare ababen more rayuwa.
Ya ƙara jaddada mahimmancin kare yara da mazauna yankin daga fuskantar wuraren gine-gine masu hadari, musamman la’akari da barkewar cutar kwalara kwanan nan. Ya ksra da cewa an yi kokarin wayar da kan jama’a tare da sanya alamomin gargadi a wurin don hana shiga da tabbatar da tsaron jama’a.
A bangaren aiwatar da aikin, Mai Gudanar da ACReSAL na Kano, Aminu Gidado, ya ce dandalin zaizayar kasa na Gayawa yana da nisa daga mita 10 zuwa 16 kuma ta kai kilomita 2.8 har zuwa inda take haduwa da Kogin Jakara.
Ya bayyana tsarin a matsayin hanyar magudanan ruwa mai mahimmanci da ke hidima ga babban vangaren birnin Kano, ciki har da GRA, Nasarawa, Tarauni, da unguwannin da ke kewaye. Ya bayyana cewa aikin ya hada da manyan gadoji 5 da ke da tazarar mita 210, 510, kilomita 2, 2.3, da 2.6, inda wasu aka tsara su don motocin.
A nasa jawabin, Hakimin Unguwar Bulbula, Buhari Isa Umar, ya ce aikin ya rage samun ayyukan laifi a yankin, duk da cewa ba a gama ba tukuna.
Ya bayyana cewa kafin a fara aikin, ’yan daba, ciki har da masu sayar da miyagun wayoyi, sukan boye su gudanar da haramtattun ayyuka a yankin.












































