Gwamna Namadi ya sauyawa kwamishinoninsa 3 ma’aikatu

Umar Namadi 750x430

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya amince da sake sauyawa kwamishinoninsa guda uku ma’aikatu a wani sauyi da ya yiwa majalisar zartarwarsa domin inganta shugabanci nagari.

Kwamishinan yada labarai, matasa, wasanni da Al’adu Sagir Musa ne ya bayyana hakan a karshen taron majalisar zartarwa ta jiha a ranar Litinin a Dutse.

Ya ce sauye-sauyen na da matukar muhimmanci domin bunkasa kokarin gwamnatin da ke da nufin tabbatar da ci gaba mai dorewa a jihar.

Wadanda abin ya shafa sun hada da Muhammad Alhassan na ma’aikatar kasa, gidaje da raya birane da tsare-tsare inda aka mayar da shi zuwa ma’aikatar albarkatun ruwa, sai Ibrahim Hanungiwa na ma’aikatar kananan hukumomi da ci gaban al’umma zuwa ma’aikatar albarkatun ruwa.

Karin karatu: Yan sanda sun kama wani matashi dan shekara 20 da ya kashe mahaifinsa a Jigawa

Yayin da Ahmed Garba ya koma ma’aikatar kananan hukumomi da ci gaban al’umma ma’aikatar filaye, gidaje, raya birane da tsare-tsare na yankin.

Musa ya ce sauye-sauyen sun fara aiki nan take, inda ya ce ana sa ran jami’an da abin ya shafa za su kai rahoto ofishinsu nan da ranar 19 ga watan Mayu (NAN).

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here