Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wani matashi dan shekara 20 da haihuwa, bisa zarginsa da kai wani mummunan harin fashi da makami da ya yi sanadin mutuwar wani matashi dan shekara 30 a unguwar Danbare da ke Kano.
SolaceBase ta ruwaito cewa an bayyana hakan ne a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar ranar Talata.
A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, 5 ga watan Mayu, 2025, da misalin karfe 6:40 na safe, inda wasu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne suka kai farmaki gidan marigayin mai suna Shehu Muhammad, inda suka caka masa wani dogon karfe mai kaifi tare da jikkata shi.
Bayan rahoton, kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya tura jami’an tsaro da jami’an bincike zuwa wurin da lamarin ya faru.
An garzaya da mamacin zuwa asibitin kwararru na Murtala Muhammad, inda wani likita ya tabbatar da rasuwarsa.
Karin karatu: Yan sanda sun kama wani matashi dan shekara 20 da ya kashe mahaifinsa a Jigawa
An kama daya daga cikin wadanda ake zargin mai suna Aliyu Umar a wurin, kuma an samu nasarar gano makamin da ake zargin an yi amfani da shi wajen kai harin.
Rundunar ‘yan sandan ta ce wanda ake zargin a halin yanzu yana taimakawa a binciken kuma za a gurfanar da shi gaban kotu bayan an kammala.
Rundunar ‘yan sandan ta kuma baiwa jama’a tabbacin ci gaba da kokarinta na wanzar da zaman lafiya da tsaro, inda ta bukaci mazauna yankin da su sanya ido tare da kai rahoto ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa ko kuma ta hanyar wayar tarho da aka sadaukar.
Karanta: Gwamna Namadi ya sauyawa kwamishinoninsa 3 ma’aikatu
Rundunar ‘yan sandan ta kuma yabawa al’ummar yankin bisa gaggauwa da suka yi wajen bayar da rahoton faruwar lamarin tare da taimaka wajen cafke wanda ake zargin.