Tsohon Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya rasu ranar Lahadi yana da shekara 82 da haihuwa.
Wata sanarwa da Garba Shehu mai magana da yawunsa ya fitar ta ce Buhari ya rasu a wani asibiti da ke birnin Landan.
Fadar shugaban Najeriya ta ce ya rasu da misalin ƙarfe 4:30 “sakamakon doguwar jinya”.
“Shugaban ƙasa ya umarci Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima ya tafi Landan domin ya rako gawar Buhari zuwa gida Najeriya,” a cewar wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa.
A makon da ya gabata ne aka kwantar da tsohon shugaban a asibiti bayan ya je duba lafiyarsa kamar yadda ya saba, amma daga baya sai ya kamu da rashin lafiya.
Sai dai Garba Shehu bai bayyana rashin lafiyar da Buhari ke fama da ita ba ko sunan asibitin da yake jinya a lokacin.
Buhari ya mulki Najeriya a matsayin zaɓaɓɓen shugaban ƙasa daga 2015 zuwa 2023, inda ya miƙa wa Bola Tinubu ragama bayan jam’iyyarsu ta APC ta sake lashe zaɓen shugaban ƙasa.













































