Cutar mashako ta kashe mutum 25 a Jihar Kano

KANO MAP 4
KANO MAP 4

Sama da mutane 25 ne suka mutu sakamakon bulkar ciwon mashako a jihar Kano.

Jaridar Solacebase ta tattaro cewa tun a ranar Juma’a 13 ga watan Janairun 2023 ne cutar wadda ke kashe kananan yara wacce aka gano ta a shekarar 2022, ta sake bulla a Kano, inda yanzu haka ake bawa wadanda suka kamu da ita kulawar gaggawa a asbitin kwararru na Murtala Muhammed da kuma asibitin koyarwa na Aminu Kano, a jihar Kano.

Kwararun likitoci sun bayyana cewa wannan cutar da ke harbar hanci da makogaro za’a iya samun kariya daga kamuwa da ita ta hanyar amfani da rigakafi wato (vaccine.)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here