Babban sifeton ‘yan sandan Najeriya, Usman Baba, ya bada umarnin kai jami’an tsaro makarantu, cibiyoyin lafiya da sauran gurare masu mahimman ci a fadin kasar nan
Bayanin haka na dauke cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, CSP Olumuyiwa, ya fitar yau Lahadi a Abuja.
Sanarwar tace, Baba ya kuma bada umarnin yin zagaye da binkice akai akai, domin dakile duk wani shiri na ta’addanci a kasar nan.
Sannan kuma ja kunnan jami’an na ‘yan sanda, da su nuna kwarewa, jajircewa da kuma bin dokokin aiki, ya yin gudanar da aikin su a fadin kasa baki daya.













































