Auren Zawarawa: Gwamnan Kebbi zai bada Naira dubu dari 180 a matsayin sadaki ga kowacce amarya

Gov. Nasir Idris Kebbi 720x430

Gwamnatin jihar Kebbi ta fara shirye-shiryen daukar nauyin daurin auren ma’aurata 300 a jihar wanda aka shirya yi a ranar 27 ga watan Fabrairu.

Shugaban kwamitin shirya taron, Alhaji Suleiman Argungu, ya shaida wa manema labarai ranar Lahadi a Birnin Kebbi cewa an shirya daurin auren ne da hadin gwiwar wata kungiya mai zaman kanta ta Nafisa Nasir Charity Development Foundation.

Ya ce an kafa kwamitoci daban-daban da ke da ayyuka na musamman kamar gwajin ciki, gwajin jini, gwajin cutar kanjamau da sauran sharuddan da suka dace na aure a jihar.

Karin karatu: Maimakon kashe Naira biliyan 2.5 domin Auren Zawarawa, kamata ya yi a duba abinda al’umma suka fi buƙata – Martanin kungiya ga gwamnati

Argungu ya ce taron daurin auren ya kasance cika alkawari ne da Gwamna Nasir Idris ya yi a lokacin daurin auren da ya gabata na cewa za a gudanar da irin wadannan bukukuwan aure lokaci-lokaci domin a taimaka wa marasa galihu su yi aure.

“Gwamnatin Gwamna Idris za ta bayar da Naira 180,000 a matsayin sadaki ga kowacce amarya daga kananan hukumomin jihar 21.

“Za a samar da wasu ƙarin abubuwa kamar kayan ɗaki da kayan abinci ga duk ma’auratan don ƙarfafa dangantakar aurensu.

“Za a daura auren ne bayan tattaunawa da malaman addinin Musulunci bisa tsarin da Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya koyar,” in ji Argungu. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here