An Kama Mai Yi Wa Masu Garkuwa Da Mutane Leken Asiri A Abuja

police 1 750x430 1
police 1 750x430 1

’Yan sanda sun samu nasarar cafke wani da ake zargi da kwarmata bayanai ga masu masu garkuwa da mutane a Abuja.

Wanda ake zargin mai shekara 25 wanda ake yi wa lakabi da Auta na daga cikin wadanda ‘yan sandan ke zargi da jigilar makamai ga masu garkuwa da mutane da suka addabi birnin Abuja.

A wata sanarwa da mai magana da yawun ‘yan sandan reshen Abuja, Josephine Adeh ta fitar, ta bayyana cewa Auta na daga cikin wadanda rundunar take nema ruwa a jallo.

“Wanda ake zargin na daga cikin wadanda rundunar ke nama, an kama shi saboda hannu a jigilar makamai da harsasai da kayan abinci da muggan kwayoyi ga masu laifi a maboyarsu daban-daban da ke cikin daji ta hanyar amfani da babur.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here