Wani faifan bidiyo da aka hango Dan takarar Shugaban kasa na jam’iyyar LP Peter Obi ya karade shafukan sada zumunta, da aka daukeshi awata hira da gidan talabijin na Channels yayi
A cikin faifan bidiyon an gano tareda jiyo Mista Obi ke yin tir da ikirarin da gwamnatin tarayya tayi na cewa masu fafutukar kafa kasar Biafra IPOB, kungiyar ta’addanci ce.
Bayan yin amanna cewa kungiyar ta IPOB ta kware wajan tada zaune tsaye a jihohin inyamurai da sauran masu ruwa da tsaki na yankunan.
Gwamnatin najeriya ta haramta ayyukan kungiyar Ipob a matsayin kungiyar ta’addanci, domin abisa doka, gwamnati na da hakki dakuma dama na assasa bin doka da oda da kama mutanen da ke da hannu ko ake zargin suna da hannu, ko goyon bayan duk wata kungiya da ke barazana ga tsaron kasa.
Duk da irin ta’asar da kungiyar ta IPOB ke yi, wadanda suka hada da raunata mutane, kashe jami’an tsaro da kuma kone-kone daban-daban da kungiyar ta yi, A ra’ayin Peter Obi, ‘yan kungiyar ta IPOB ba ‘yan ta’adda ba ne.
“Abin dake akwai kawai shine sa6a dokar kasa da Akayi na kiran su ‘yan ta’addar IPOB, dan haka su ba ‘yan ta’adda ba ne. Na san su, ina zaune tare da su”.
Gwamnatin Najeriya ta haramta ayyukan kungiyar ta IPOB amma duk da haka, shugabanta Nnamdi Kanu ya ci gaba da matsa kaimi wajen ganin sun cimma manufar su ta neman ballewa daga kasa Najeriya. Bayan da suka tafka barna da ta’annati mai tarin yawa, Daga bisani Nnamdi Kanu ya tsere yabar kasar d’ungurungun, lokacin da jami’an tsaron Najeriya suka yi kokarin kama shi a watan Satumbar na 2017.
Amma abisa kokarin da kasashen duniya suka yi da hukumomin tsaro, aka kamo Kanu awata kasa tareda maido dashi Najeriya.
Tun daga wancan lokaci Mista Kanu da wadanda ke dafa masa suke fuskantar tuhumar cin amanar kasa daga babbar kotun tarayya da ke Abuja.
Da yake jawabi ga manema labarai kan ta’addancin kungiyar da IPOB keyi, babban lauyan gwamnatin tarayya Abubakar Malami ya ce ‘yan awaren na daukar makamai kuma sun kashe jami’an tsaro kusan 175, da kuma wasu manyan mutane tsakanin Oktoba 2020 zuwa Yuni 2021.
“A ranar 21 ga Oktoba, 2020 , Nnamdi Kanu ta cikin wani shirin rediyon da ake kiran way kai tsaye ta yanar gizo (Radio Biafra), ya zaburar da ‘yan kungiyar ta IPOB da su kona dukkanin ofisoshin ‘yan sanda tare da kashe jami’an tsaron gwamnati, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an tsaro da dama tare da lalata dukiyoyin jama’a da na masu zaman kansu.
Kungiyar IPO dake da sansani a kudu maso Gabashin kasar nan ta kashe jami’an tsaro 175 wadanda suka hada da ‘yan sanda 128 da sojoji 37 da wasu jami’an tsaro 10.” Inji Malami.
Sai dai duk hakan, Peter Obi be yi la’akari da hakan ba, bai ga alamun wani kuskure a cikin ta’annati da su Kanu suke yi ba. Hasali ma, Peter Obi na matukar goyon bayan matakin da ‘yan uwansa suka dauka a kungiyar ta IPOB.
Bala brahim, Daraktan Yada Labarai na jam’iyyar APC ne ya rubuta daga Abuja.












































