Kisan plateau: Sojoji sun fara tsayarwa tare da bincike a jos, sun kama wadanda ake zargi

Plateau killings 750x430

Dakarun sojin ƙasar nan karkashin rundunar “Operation Enduring Peace” sun fara wani gagarumin aikin tsayarwa da bincike a fadin birnin jos.

Jami’in yada bayanai na rundunar kaptin chinonso polycarp oteh, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa, inda ya ce an fara aikin ne tun ranar juma’a.

Ya ce wannan mataki na daga cikin kokarin dawo da cikakken zaman lafiya tare da tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi a fadin jihar plateau.

Sanarwar ta bayyana cewa karuwar tsaro da aka girka ta haifar da sakamako nan take, inda sojoji suka kama mutane biyu da ake zargi tare da kwato wata bindiga kirar ak-47 da aka kera a gida, da harsasai guda hudu na nau’in 7.62 milimita da kuma wata bindiga mai harbi ta famfo.

Ya kuma bayyana cewa kamen da kwace makaman sun faru ne yayin ayyukan bincike da aka mayar da hankali a wuraren da ake yawan tashin hankali da hanyoyin wucewa, ciki har da arewacin jos da kudancin jos, dadinkowa, mahadar tsohon filin jirgin sama, tudun wada da kuma gidajen gwamnati na masu karamin karfi.

A wani bangare kuma, sojojin sun yi gaggawar amsa kiran neman agaji kan harbe-harbe da aka ruwaito a yankin kasuwar shanu ta yelwa a karamar hukumar shendam.

Da zuwan sojojin, maharan da ba a san ko su wanene ba sun tsere zuwa cikin dazuka sakamakon matsin lambar da suka fuskanta daga dakarun.

Bayan haka, yayin binciken yankin, sojojin sun gano wasu mazauna yankin guda biyu da suka samu raunukan harbi, inda aka garzaya da su zuwa asibiti domin samun kulawar gaggawa.

Rundunar sojin ƙasa ta sake jaddada kudurinta na tabbatar da cikakken tsaro a fadin jihar plateau, tana mai cewa za ta ci gaba da karfafa wannan aiki har sai an kawar da duk wata barazanar tashin hankali tare da dawo da zaman lafiya mai dorewa a dukkan yankunan da abin ya shafa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here