zargin zamba: Kotu ta bada umarnin kamo ‘yan kasar waje biyu

Nabil Maukarzel and Halawi Fidaa
Nabil Maukarzel and Halawi Fidaa

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Lagos, ta bada umarnin kamo wasu ‘yan kasar waje da suke gudanar da kasuwancin su a Najriya, Nabil Maukarzel da kuma Halawi Fidaa bisa kin bin umarnin kotun na su bayyana a gabanta tun 2021, kan zargin damfara wace ta kai kimanin biliyan N9.4.

Ana zargin Maukarzel, wanda dan Labanan ne da kuma Fidaa dan kasar faransa bisa mallakr kudin damfara wanda suka kai N9,442, 788,578.93, a bankin ECO Bank.

Kuton bada umarnin cewa duk inda aka gansu, a kamasu a kai su ofishin ‘yan sanda mafi kusa.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here