Gwamnatin tarayya ta dakatar da dalibai 13 na kwalejin gwamnatin tarayya dake jihar Enugu na tsawon makwanni shida bisa zargin cin zarafi a makarantar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa a Abuja ranar Laraba ta hannun daraktan yada labarai da hulda da jama’a a ma’aikatar, Folashade Boriowo.
Ministan Ilimi, Dr Tunji Alausa ya bayar da umarnin dakatar da daliban bisa wani faifan bidiyo da ya nuna wasu daliban makarantar na cin zarafi.













































