Yajin aikin PASAN: Ma’aikata Sun Rufe Majalisa A Sokoto

PASAN Sokoto State Executive led by Mr Abubakar Yusuf as they shut State House of Assembly entrance on Monday
PASAN Sokoto State Executive led by Mr Abubakar Yusuf as they shut State House of Assembly entrance on Monday

Mambobin kungiyar ma’aikatan majalisar dokokin Najeriya reshen jihar Sokoto (PASAN) a ranar Litinin sun bi sahun takwarorinsu na kasa baki daya a yayin da suka shiga yajin aiki na sai baba ya gani, tare da rufe harabar majalisar dokokin jihar.

Shugaban kungiyar, Abubakar Yusuf, yayin da yake zantawa da manema labarai a Sokoto ya bayyana cewa yajin aikin wani tsawaita fafutuka ne da suka fara a shekarar 2020.

Ya ce, “Kamar yadda za ku iya tunawa, mun dauki irin wannan matakin ne a shekarar 2020. Bayan shiga tsakani daga bangarori daban-daban, mun cimma yarjejeniya da ta yi alkawarin ba da cikakken ‘yancin cin gashin kai ga bangaren majalisar dokoki.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here