Wani Mamba a Majalisar wakilan tarayya Nse Ekpenyong ya rasu

Nse Ekpenyong
Nse Ekpenyong

Dan-majalisar wakilan tarayya mai wakiltar Mazabar Oron a majalisar tarayya, Nse Ekpenyong, ya mutu.

An rawaito Mista Ekpenyong, mai shekaru 58, ya mutu ne a ranar Asabar.

Shugaban Karamar hukumar Mbo a jihar Akwa-Ibom, Asuqwo Eyo, shi ne ya tabbatar da mutuwarsa a ranar Litinin.

Yace kafin rasuwar Mista Ekpenyong bai kwanta rashin Lafiya ba.

Shi dai Mistw Ekpenyong kafin rasuwarsa yana wakilitar mazabar Oron a Majalisar Tarayya daga jihar Akwa-lbom ne, kuma zai kammala wa’adin Zango na biyu ne a Majalisar cikin watan Mayun shekarar 2023.

Kazalika tsohon Mamba ne a majalisar dokokin jihar Akwa Ibom, kuma tsohon mataimakin shugaban Jam’iyyar PDP na Jihar.

Kafin shigarsa harkokin siyasa ya yi aiki matsayin Manajan Darakta a kamfanin Based/Investment Trust Co Nigeria Ltd daga baya kuma ya zama mamallakin kamfanin Brule Integrated Nigeria Ltd.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here