Hukumar gudanarwar jami’ar Legas (UNILAG) ta sanar da rage kudin makaranta bayan ganawa da wakilan kungiyar dalibai ta kasa (NANS) a ranar Alhamis.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a safiyar Juma’a.
Sanarwar ta bayyana cewa jami’ar ta gudanar da taro da shuwagabannin NANS da sauran malaman jami’ar a yammacin ranar Alhamis.












































