Tinubu ya nada sabbin manyan Sakatarori 2

tinubu 2 (2)

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin sabbin manyan sakatarori guda biyu don cike guraben da ake da su a ma’aikatan gwamnatin tarayya.

Eno Olotu, daraktar yada labarai da hulda da jama’a, ofishin shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ce (HCSF) ta sanar da hakan a wata sanarwa da ta fitar a Abuja ranar Laraba.

Sabbin jami’an da aka nada sun hada da Adeladan Olarinre da Mukhtar Muhammed.

Karanta: Tinubu ne yaƙi amincewa da naɗi na a matsayin minista, ba majalisar dattawa ba – El-Rufai

Olotu ta ce nadin ya biyo bayan zabar wanda ya yi daidai da jajircewar gwamnatin da cancanta har ma da kwarewa a aikin gwamnati.

Ta kara da cewa nade-naden da aka yi na nuna himmar da gwamnatin ta yi na samar da ingantacciyar gwamnati mai dogaro da kai wanda ya dace da bukatun ‘yan Najeriya. (NAN)

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here