Tinubu Ya Gana Da Akpabio Da Jonathan A Aso Rock

Tinubu and Jonathan 750x430 1
Tinubu and Jonathan 750x430 1

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu yanzu haka yana ganawa sabon Shugaban Majalisar Dattajai, Godswill Akpabio, a fadarsa ta Aso Rock da ke Abuja.

Kazalika, cikin tattaunawar akwai Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma da tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje.

Shi ma Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu na tare da su a tattaunawar.

Gabanin haka, Shugaba Tinubu ya kuma gana da tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan a ofishinsa.

Sai dai har yanzu babu cikakken bayani game da makasudin duka ganawar tasu.

Shi ma shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya gana da Tinubun.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here