Taron jam’iyya: Abdulrahaman Mohammed ya zama shugaban PDP na kasa

Abdulrahaman Mohammed PDP National Chairman 1

Abdulrahaman Mohammed ya zama shugaban jam’iyyar PDP na kasa a babban taron jam’iyyar da aka gudanar a Abuja ranar Lahadi.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN ya rawaito cewa Mohammed tare da sauran sabbin mambobin kwamitin gudanarwa na kasa NWC an zabe su ne ta hanyar amincewa da juna domin jagorantar jam’iyyar na tsawon shekaru hudu masu zuwa.

Mambobin sabon NWC kamar yadda shugaban kwamitin zaben taron, Farfesa Sandy Onor, ya sanar sun hada da Aaron Chukwuemeka a matsayin mataimakin shugaban kasa (kudu) da Yusufu Akirikwen, SAN, a matsayin mataimakin shugaban kasa (arewa).

Haka kuma Samuel Anyanwu ya zama sakataren kasa, Kolawole Olabisi mataimakin sakataren kasa, Diran Odeyemi ma’aji na kasa da Lado Mark mataimakin ma’aji.

Sauran sun hada da Eyim Henry a matsayin sakataren kudi na kasa, Dokta Grema Kyari mataimakin sakataren kudi, Umar Bature sakataren tsare-tsare da Efere Augustine mataimakin sakataren tsare-tsare.

Haka kuma Jungudo Mohammed ya zama sakataren yada labarai na kasa, Egwu Chidiebere mataimakinsa, Kamaldeen Ajibade mai ba da shawara kan shari’a da Aloysius Uba mataimakinsa.

Osuoha Donatus ya zama mai binciken kudi na kasa, Dokta Adaba Yatu mataimakinsa, Farfesa Ogunshe Adedayo shugabar mata ta kasa da Hauwa Shinge mataimakiyarta.

Ibrahim Aboki ya zama shugaban matasa na kasa, yayin da Momoh Bashir ya zama mataimakinsa.

Kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN ya rawaito cewa an rantsar da sabbin mambobin NWC nan take bayan kammala zaben.

A jawabinsa na karbar mukami, sabon shugaban jam’iyyar na kasa, Mohammed, ya yi alkawarin ba zai bai wa jam’iyyar kunya ba.

Ya kuma tabbatar da cewa sabon kwamitin zai hada kai da shugabannin jam’iyyar domin karfafa hadin kai da kuma shirya PDP domin samun nasara a zaben shekarar 2027.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here