Tambuwal ya zargi Tinubu da ruguza jam’iyyun adawa

R L Bola Tinubu and Aminu Tambuwal 750x378

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, ya zargi shugaba Bola Tinubu da jam’iyyar APC mai mulki da ruguza ‘yan adawa.

Tambuwal yayi wannan zargi a ranar Juma’a lokacin da aka nuna shi a gidan Talabijin na Channels a shirin Siyasa a yau, yana mai ikirarin cewa da gangan APC da Tinubu suka shirya faduwar jam’iyyun adawa a kasar.

“Idan ka kalli abin da ke faruwa a jam’iyyun siyasa daban-daban a Najeriya a yau – ba ka bukatar a gaya maka, ko da kuwa yawan musun da kowa ya yi, ciki har da shugaban kasa Bola Tinubu, cewa ba su da hannu a yunkurin tada zaune tsaye na jam’iyyun adawa,” in ji Tambuwal a kan al’amuran yau da kullum.

“Ba wai ina zarginsu bane, ina cewa suna da hannu a yunkurin da ake yi na kawo cikas ga jam’iyyun adawa,” in ji shi

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here