Sojoji sun hallaka ƴan bindiga 23 da ke shirin tserewa daga Kano bayan hare-haren da suka kai cikin dare

IMG 20260104 WA0011 750x430

Aƙalla ƴan bindiga 23 ake zargin an hallaka su a wani aikin haɗin gwiwar soji bayan wasu ƙungiyoyin masu makamai sun kai hare-hare a ƙananan hukumomin Shanono da Tsanyawa na Jihar Kano tsakanin daren 1 ga Janairu zuwa safiyar 2 ga Janairu, 2026, kamar yadda rundunar sojin Najeriya ta bayyana.

Wannan na cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar Soji, Brigade ta 3, Manjo Babatunde Zubairu, ya fitar a ranar Lahadi, inda ya ce aikin ya haɗa da dakarun rundunar haɗin gwiwa a ƙasa da kuma sashen sama na Aikin FANSAN YAMMA.

Sanarwar ta nuna cewa dakarun sun yi nasarar dakile hare-haren a Kano tare da jawo asara mai yawa ga maharan, kafin su bi sawun ‘yan fashin da suka tsere zuwa ƙauyen Karaduwa da ke Ƙaramar Hukumar Matazu a Jihar Katsina da ke makwabtaka da Kano.

Bisa sahihin bayanan sirri, sashen sama ya ci gaba da binsu yayin da suke ƙoƙarin sake haɗuwa bayan sun tsere daga Kano.

Rundunar sojin ta ce rahotannin sirri sun nuna cewa ‘yan fashin suna cikin shirin binne wasu daga cikin mutanensu da aka kashe a artabun farko, lokacin da aka gano su a Dan Marke a Ƙaramar Hukumar Matazu.

Sashen sama na Sashe na 2 na Aikin FANSAN YAMMA ya bibiyi motsinsu har zuwa lokacin da aka ga babura da dama sun taru bayan ketare wani busasshen kogi, inda nan take aka kai farmakin sama mai inganci, tare da goyon bayan sa ido da tattara bayanan sirri daga sama.

Jaridar Solacebase ta rawaito cewa farmakin, a cewar rundunar sojin, ya yi sanadiyyar hallaka aƙalla ‘yan ta’adda 23, yayin da ake zargin wasu da dama sun jikkata, tare da lalata makamai da sauran kayan aikinsu.

Rundunar sojin ta ƙara da cewa halin tsaro a Jihar Kano yana nan cikin kwanciyar hankali, inda dakarun ke ci gaba da sintiri mai ƙarfi da sa ido kan wuraren da ake ganin barazana.

Ta kuma yi kira ga jama’a da su ci gaba da ba hukumomin tsaro sahihan bayanai a kan lokaci domin taimakawa wajen murƙushe ‘yan fashi da sauran ayyukan ta’addanci.

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here