Shettima ya dawo Abuja bayan halartar taron MDD karo na 80 da kuma ganawa a Jamus

Shettima Returns

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, ya dawo Abuja bayan wata nasarar tafiyar diflomasiyya da ya wakilci shugaban kasa Bola Tinubu a taron Majalisar Dinkin Duniya karo na 80 da aka gudanar a birnin New York, tare da kammala wasu muhimman hulɗoɗi a Jamus.

A yayin taron, Shettima ya gabatar da jawabin ƙasa na shugaba Tinubu, inda ya bukaci a gudanar da sauye-sauye masu zurfi a tsarin Majalisar Dinkin Duniya.

Haka kuma, ya tsaya tsayin daka wajen kare ikon nahiyar Afrika kan albarkatun ma’adinai da darajarsu ta kai dala biliyan 700.

Mataimakin shugaban kasar ya kuma yi amfani da damar wajen ƙarfafa alaƙa da Birtaniya, Gidauniyar Gates da sauran abokan hulɗar ƙasa da ƙasa.

Bugu da ƙari, ya gana da babban sakataren MDD, António Guterres, wanda ya yaba da matsayar Najeriya kan neman kujerar dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar.

A wani bangare na tarukan, Shettima ya gabatar da damar da Najeriya ke da ita na sauyin makamashi da aka kiyasta kimarta a kan dala biliyan 200 ga masu zuba jari na duniya.

Wannan ya kasance wani muhimmin mataki na jawo hankalin masu saka hannun jari wajen tallafa wa tattalin arzikin ƙasar.

Haka zalika, ya tabbatar wa ‘yan Najeriya mazauna ƙasashen waje cewa gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da kula da su tare da tabbatar musu da cikakken haɗin kai a manufofi da shirye-shiryen ci gaba na gwamnati.

Bayan kammala waɗannan ayyuka a birnin New York, Shettima ya zarce Jamus, inda ya yi wasu muhimman ganawa kafin komawarsa Abuja. Wannan tafiya ta ƙara bayyana matsayin Najeriya a idon duniya da kuma ƙudirin gwamnatin Tinubu na samun goyon bayan ƙasashen waje wajen tafiyar da manufofinta.

 

AYI TSOKACI

Please enter your comment!
Please enter your name here